Matthew 1

Asalin Yesu

1Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim:

2Ibrahim ya haifi Ishaku,

Ishaku ya haifi Yaƙub,
Yaƙub ya haifi Yahuda da ʼyanʼuwansa,
3Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu;
Ferez ya haifi Hezron,
Hezron ya haifi Ram,
4Ram ya haifi Amminadab,
Amminadab ya haifi Nashon,
Nashon ya haifi Salmon,
5Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa,
Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa,
Obed ya haifi Yesse,
6Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda.
Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.

7Solomon ya haifi Rehobowam,
Rehobowam ya haifi Abija,
Abija ya haifi Asa,
8Asa ya haifi Yehoshafat,
Yehoshafat ya haifi Yehoram,
Yehoram ya haifi Azariya,
9Azariya ya haifi Yotam,
Yotam ya haifi Ahaz,
Ahaz ya haifi Hezekiya,
10Hezekiya ya haifi Manasse,
Manasse ya haifi Amon,
Amon ya haifi Yosiya,
11Yosiya kuma ya haifi Yekoniya
Wato, Jehohiyachin; haka ma a aya 12
da ʼyanʼuwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.
12Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon:

Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel,
Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,
13Zerubbabel ya haifi Abiyud,
Abiyud ya haifi Eliyakim,
Eliyakim ya haifi Azor,
14Azor ya haifi Zadok,
Zadok ya haifi Akim,
Akim kuma ya haifi Eliyud,
15Eliyud ya haifi Eleyazar,
Eleyazar ya haifi Mattan,
Mattan ya haifi Yaƙub,
16Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.
17Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka, daga lokacin Ibrahim zuwa Dawuda; zuriya goma sha huɗu daga lokacin Dawuda zuwa lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon, saʼan nan zuriya goma sha huɗu kuma, daga lokacin kwasa zuwa bauta a Babilon har zuwa kan Kiristi.
Ko kuwa Almasihu. “Kiristi” (Da Helenanci) “Almasihu” (Da Ibraniyanci) duk suna nufin “Shafaffe.”


Haihuwar Yesu Kiristi

18Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance: An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf, amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 19Yusuf mijinta kuwa da yake shi mai adalci ne, bai so yǎ ba ta kunya, yǎ tone mata asiri a fili ba, ya yi tunani yǎ sake ta a ɓoye.

20Amma bayan yanke wannan shawara, sai wani malaʼikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki, ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne. 21Za ta haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu,
Yesu da Helenanci shi ne Yoshuwa da Ibraniyanci, wanda yake nufin Ubangiji yana ceto.
gama shi zai ceci mutanensa daga zunubansu.”

22Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabi cewa, 23“Ga shi budurwa za ta yi ciki, za ta haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel,” 
Ish 7.14
— wanda yake nufin, “Allah tare da mu.”

24Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin malaʼikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa. 25Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.

Copyright information for HauSRK